fidelitybank

Artabu: ‘Yan ta’adda 38 sun mutu ciki harda ‘yan sanda 5 – ‘Yan Sanda

Date:

Akalla ‘yan ta’adda 38 ne a ke zargi an kashe yayin da jami’an ‘yan sanda biyar su ka rasa ransu a wani arangama da a ka yi da juna daban-daban a jihar Katsina a shekarar 2021.

Kwamishinan ‘yan sanda jihar Katsina, Sanusi Buba ya bayyana hakan ne yayin wani taron ‘yan jarida na musamman.

Kwamishinan wanda ya samu wakilcin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya koka da ayyukan ‘yan ta’adda a jihar.

Ya ce “Hakika, ba shakka lokaci ne mai wahala, rundunar ta samu gagarumar nasara a kan barazanar ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da makami da sauran nau’ikan laifuka da aikata laifuka a jihar. Shekarar 2021 ta samu a cikin raguwar yawan laifuka a jihar idan a ka kwatanta da shekarar da ta gabata.”

“A yayin wannan artabun, an kashe ‘yan bindiga talatin da takwas (38) a fadan bindigu daban-daban yayin da jami’an ‘yan sanda biyar (5) suka biya su ka rasa ransu,” inji shi.

Kwamishinan ya ce, rundunar ta kama mutane 999 da a ke zargi da aikata laifuka 608 da a ka samu. Yayin da adadin wadanda a ka kama 874 ke fuskantar shari’a a kotunan shari’a daban-daban na jihar.

Ya kara da cewa an kama jimillar mutane 157 da a ke zargin ‘yan fashi da makami ne, sannan 145 daga cikinsu an gurfanar da su gaban kotu yayin da 12 ke ci gaba da bincikar su.

“An kama masu garkuwa da mutane sittin da biyar sannan an gurfanar da 63 a gaban kotu yayin da biyu ke kan bincike.”

Ya kuma ce,”An kama mutane 244 da a ke zargin barayin shanu ne, daga cikinsu an gurfanar da wadanda a ke zargin 230 a gaban kotu yayin da 14 ke ci gaba da bincikar su. An kwato dabbobin gida guda 1,243 wadanda su ka hada da shanu 867, tumaki 352, awaki 24 da jaki daya daga cikin mazubin”. A cewar sanarawar.

Kwamishinan ya ce an kama mutane 246 da ake zargi a cikin 195 da aka samu na fyade da kuma laifukan da suka saba wa ka’ida inda ya ce an kubutar da mutane 63 da aka yi garkuwa da su a wasu shari’o’i hudu da aka samu na fataucin bil adama da aka kai ofishin NAPTIP na jihar Kano.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp