fidelitybank

Gwamnati ta kawo karshen kisan gillar da a ke yi wa ‘yan Najeriya – Sheikh Dahiru Bauchi

Date:

Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya bukaci gwamnatin tarayya ta yi duk mai yiwuwa wajen kawo karshen ayyukan ’yan ta’addar da su ka addabi Najeriya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya kuma bayyana wajibcin gwamnati ta fitar da ’yan Najeriya daga halin tsoron da suke ciki, a lokacin da ya ke jawabi a majalisinsa, inda ya bayyana takaicinsa kan halin rashin tsaron da Najeriya ke ciki.

Ya bayyana cewa, “Ba mu zabe su don mu zama haka ba, ba mu zabe su don mu zama abin tausayi irin wannan ba, ya zama ana kashe mu ba mai kariya ana sayar da mu kamar dabbobi — ana yin abin da aka ga dama da mu — alhali muna da gwamnatoci har guda uku a kanmu; Wannan abin kunya ne, abin dariya ne, abin kuka ne”.

Jawabin malamin na zuwa ne kwanaki kadan bayan kisan gillar da ’yan bindiga suka yi wa sama da mutun 30 a Sabon Birni a Jihar Sokoto, wanda ya haifar da zanga-zanga a Arewacin Najeriya.

’Yan bindiga sun dauki tsawon lokaci suna kashe-kashe da garkuwa da mutane domin karbar kudaden fansa, gami da yi wa mata fyade da kona garuruwa da dukiyoyi da sauran na’uikan ta’addanci, musamman a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya ce, “Abin da yake wajibi ga gwamnatoci [shi ne] su kula su fitar da mu daga abin da muke ciki na tsoro —kana gidanka kana jin tsoro, kana waje kana jin tsoro, kana tafiya kana jin tsoro, alhali akwai gwamnatoci har guda uku a kanka.”

“Duk muna daura muku nauyi na kuwala da rayukan jama’ar Najeriya da zaman lafiyar Najeriya da walwalar Najeriya; Ina aka ce kasa ko noma ba za a yi ba, to me za a ci?”

Ya yaddada kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi da kananan hukumomi su tashi tsaye, domin yin duk abin da ya dace wajen samar da tsaro da kuma sauke duk nauyin da kundin tsarin mulki ya rataya a wuyansu na kare rayuka da dukiyoyi da kuma jin dadin al’ummar kasa. A cewar Aminiya.

 

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp