fidelitybank

Gwamnati ta kawo karshen kisan gillar da a ke yi wa ‘yan Najeriya – Sheikh Dahiru Bauchi

Date:

Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya bukaci gwamnatin tarayya ta yi duk mai yiwuwa wajen kawo karshen ayyukan ’yan ta’addar da su ka addabi Najeriya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya kuma bayyana wajibcin gwamnati ta fitar da ’yan Najeriya daga halin tsoron da suke ciki, a lokacin da ya ke jawabi a majalisinsa, inda ya bayyana takaicinsa kan halin rashin tsaron da Najeriya ke ciki.

Ya bayyana cewa, “Ba mu zabe su don mu zama haka ba, ba mu zabe su don mu zama abin tausayi irin wannan ba, ya zama ana kashe mu ba mai kariya ana sayar da mu kamar dabbobi — ana yin abin da aka ga dama da mu — alhali muna da gwamnatoci har guda uku a kanmu; Wannan abin kunya ne, abin dariya ne, abin kuka ne”.

Jawabin malamin na zuwa ne kwanaki kadan bayan kisan gillar da ’yan bindiga suka yi wa sama da mutun 30 a Sabon Birni a Jihar Sokoto, wanda ya haifar da zanga-zanga a Arewacin Najeriya.

’Yan bindiga sun dauki tsawon lokaci suna kashe-kashe da garkuwa da mutane domin karbar kudaden fansa, gami da yi wa mata fyade da kona garuruwa da dukiyoyi da sauran na’uikan ta’addanci, musamman a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya ce, “Abin da yake wajibi ga gwamnatoci [shi ne] su kula su fitar da mu daga abin da muke ciki na tsoro —kana gidanka kana jin tsoro, kana waje kana jin tsoro, kana tafiya kana jin tsoro, alhali akwai gwamnatoci har guda uku a kanka.”

“Duk muna daura muku nauyi na kuwala da rayukan jama’ar Najeriya da zaman lafiyar Najeriya da walwalar Najeriya; Ina aka ce kasa ko noma ba za a yi ba, to me za a ci?”

Ya yaddada kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi da kananan hukumomi su tashi tsaye, domin yin duk abin da ya dace wajen samar da tsaro da kuma sauke duk nauyin da kundin tsarin mulki ya rataya a wuyansu na kare rayuka da dukiyoyi da kuma jin dadin al’ummar kasa. A cewar Aminiya.

 

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...
X whatsapp