Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayar da tallafin karatu na digiri na farko ga dalibai 16 da su ka lashe muhawarar makarantun shugaban kasa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan, Rafiu Ajakaye ya fitar a Ilorin a ranar Juma’a.
Sanarwar ta ce daliban da su ka yi fice a gasar sun sake karfafa kwarin gwiwa kan tsarin makarantun gwamnati a jihar.
Sanarwar ta yi alkawalin ci gaba da saka hannun jarin gwamnatin jihar, domin bunkasa jarin dan Adam.
Ya kuma yabawa daliban makarantun gwamnati bisa wannan kwazon da ya zama na farko a tarihin jihar.
Sanarwar ta ce gwamnatin jihar da al’ummar jihar Kwara suna alfahari da daliban da malamansu da hukumomin jihar Kwara da hukumar ilimin bai daya a jihar da kuma iyayensu .
Sanarwar ta bukaci jama’a da masu ruwa da tsaki da su marawa gwamnatocin jihohin baya bisa kokarin da su ke yi a fannin ilimi.