Wacce ta lashe gasar Miss Nigeria gasar kwalliya ta mata kyau ta 2021, Shatu Garko, ta mayar da martani kan sukar da a ka yi mata game da halartar gasar kwalliya ta bana.
A kwanan baya Garko, wadda ‘yar Kano ce, ta zama ‘yar takara na farko da ta fara sanye da hijabi da ta lashe kambun da a ke so tun bayan da a ka fara gasar a shekarar 1957.
Duk da haka, kasancewarta a gasar ta ci gaba da haifar da cece-kuce, saboda addininta na Musulunci.
Da ta ke magana a wata hira da BBC Pidgin, matashiyar mai shekaru 18 ta caccaki masu sukan ta ta na mai cewa “Yan Najeriya na son yanke hukunci da kan su”. A cewar Shatu Garko.
Sabuwar Miss Nigeria ta kuma musanta ikirarin da wasu mutane ke yi na cewa ta biya, domin ta zama zakara a gasar.
“Gaskiya ’yan Najeriya suna son yin hukunci a kan mutane. Jama’a da dama sun ce shugaban kasa ne ya biya ni domin in samu rawanin, wasu kuma sun ce gwamnan jihar ya biya ya bani rawani. Akwai kuma wadanda su ka ce iyayena sun biya Miss Nigeria, amma hakan ba gaskiya ba ne,” inji ta.
Da ta ke magana kan ikirarin Hisbah, Garko ta bayyana cewa har yanzu ba a gayyace ta ba, amma ta sha samun kalamai masu zafi daga mutane.
Sai dai samfurin hijabi, ta bayyana cewa har yanzu ba ta damu da sukar da a ke mata ba, ta kara da cewa babu wani abu da za ta iya yi game da kambun.
“Babu wanda ya kira ni amma na sami maganganu da yawa da cewa ‘Na kasance tsirara’, ‘Ina yin abin da bai dace ba,” inji Shatu.