fidelitybank

Ganduje ya yi ayyukan da za yaba masa – Fashola

Date:

Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola, ya yabawa gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje kan tallafin da gwamnatin jihar ke baiwa ayyukan gwamnatin tarayya a jihar.

Ministan ya yi wannan yabon ne a yayin ziyarar ban girma da ya kai wa gwamnan yayin da ya kai ziyarar duba ayyukan gwamnatin tarayya a jihar.

A cewar Fashola, ya na jihar ne da sauran abubuwan da zai shiga cikin shirin matasa na jam’iyyar APC na kasa da aka shirya yi a Kano a ranar 27 ga watan Janairu.

Ya ce, “Abu na biyu na ziyarar tasa shi ne duba dukkan ayyukan da gwamnatin tarayya ke gudanarwa da suka hada da shirin samar da gidaje da hanyoyin da ake ginawa a Kano da kewaye.

“Dole in godewa mai girma Gwamna bisa irin hadin kan da ma’aikatar ta samu daga Gwamnatin Jihar Kano a karkashin ikon ku. Na tabbata ayyukanmu a Kano da kewaye zai yi wahala idan ba tare da hadin kan da kuka ba mu ba. Ina mika godiyar ma’aikatar mu da ta gwamnatin tarayya.

“Daya daga cikin wuraren da muka fara jin hannun zumuncin gwamnatin jihar Kano, shi ne a bangaren shirin samar da gidaje na matukan jirgi na kasa. Shekaru da yawa baya, mun sami damar samun fili a tsakiyar birnin don shirin.

“Ba wannan kadai ba, mun sami damar kammala kashi na daya da biyu na ayyukan, an kuma ba mu filayen da zai ba mu damar fadada zuwa kashi na uku. Na zo wurin domin ganin abubuwa da kaina, kashi biyu na farko sun shirya domin fara aiki,” in ji Fashola.

Ya bukaci mazauna Kano da su yi rajistar rukunin gidajen ko dai ta hanyar siya ko kuma su samu gidajen haya.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...
X whatsapp