Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola, ya yabawa gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje kan tallafin da gwamnatin jihar ke baiwa ayyukan gwamnatin tarayya a jihar.
Ministan ya yi wannan yabon ne a yayin ziyarar ban girma da ya kai wa gwamnan yayin da ya kai ziyarar duba ayyukan gwamnatin tarayya a jihar.
A cewar Fashola, ya na jihar ne da sauran abubuwan da zai shiga cikin shirin matasa na jam’iyyar APC na kasa da aka shirya yi a Kano a ranar 27 ga watan Janairu.
Ya ce, “Abu na biyu na ziyarar tasa shi ne duba dukkan ayyukan da gwamnatin tarayya ke gudanarwa da suka hada da shirin samar da gidaje da hanyoyin da ake ginawa a Kano da kewaye.
“Dole in godewa mai girma Gwamna bisa irin hadin kan da ma’aikatar ta samu daga Gwamnatin Jihar Kano a karkashin ikon ku. Na tabbata ayyukanmu a Kano da kewaye zai yi wahala idan ba tare da hadin kan da kuka ba mu ba. Ina mika godiyar ma’aikatar mu da ta gwamnatin tarayya.
“Daya daga cikin wuraren da muka fara jin hannun zumuncin gwamnatin jihar Kano, shi ne a bangaren shirin samar da gidaje na matukan jirgi na kasa. Shekaru da yawa baya, mun sami damar samun fili a tsakiyar birnin don shirin.
“Ba wannan kadai ba, mun sami damar kammala kashi na daya da biyu na ayyukan, an kuma ba mu filayen da zai ba mu damar fadada zuwa kashi na uku. Na zo wurin domin ganin abubuwa da kaina, kashi biyu na farko sun shirya domin fara aiki,” in ji Fashola.
Ya bukaci mazauna Kano da su yi rajistar rukunin gidajen ko dai ta hanyar siya ko kuma su samu gidajen haya.