fidelitybank

Ganduje ya yi ayyukan da za yaba masa – Fashola

Date:

Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola, ya yabawa gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje kan tallafin da gwamnatin jihar ke baiwa ayyukan gwamnatin tarayya a jihar.

Ministan ya yi wannan yabon ne a yayin ziyarar ban girma da ya kai wa gwamnan yayin da ya kai ziyarar duba ayyukan gwamnatin tarayya a jihar.

A cewar Fashola, ya na jihar ne da sauran abubuwan da zai shiga cikin shirin matasa na jam’iyyar APC na kasa da aka shirya yi a Kano a ranar 27 ga watan Janairu.

Ya ce, “Abu na biyu na ziyarar tasa shi ne duba dukkan ayyukan da gwamnatin tarayya ke gudanarwa da suka hada da shirin samar da gidaje da hanyoyin da ake ginawa a Kano da kewaye.

“Dole in godewa mai girma Gwamna bisa irin hadin kan da ma’aikatar ta samu daga Gwamnatin Jihar Kano a karkashin ikon ku. Na tabbata ayyukanmu a Kano da kewaye zai yi wahala idan ba tare da hadin kan da kuka ba mu ba. Ina mika godiyar ma’aikatar mu da ta gwamnatin tarayya.

“Daya daga cikin wuraren da muka fara jin hannun zumuncin gwamnatin jihar Kano, shi ne a bangaren shirin samar da gidaje na matukan jirgi na kasa. Shekaru da yawa baya, mun sami damar samun fili a tsakiyar birnin don shirin.

“Ba wannan kadai ba, mun sami damar kammala kashi na daya da biyu na ayyukan, an kuma ba mu filayen da zai ba mu damar fadada zuwa kashi na uku. Na zo wurin domin ganin abubuwa da kaina, kashi biyu na farko sun shirya domin fara aiki,” in ji Fashola.

Ya bukaci mazauna Kano da su yi rajistar rukunin gidajen ko dai ta hanyar siya ko kuma su samu gidajen haya.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp