Kungiyar fafutukar rajin kare al’umma ta Umbrella of Kano Concerned Civil Society Groups, ta yi kira ga Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da ya gaggauta korar Manajan Daraktan Hukumar Kula da Zairga-zairgar ababan hawa ta KAROTA, Baffa Babba Dan Agundi.
Kungiyar ta kuma bukaci Gwamnati da ta kafa kwamitin bincike, domin gano hakikanin kudaden shigar da a ka ce hukumar na tarawa.
Da ya ke ganawa a taron masu ruwa da tsaki jihar, a yammacin ranar Talata, shugaban kungiyar na jihar, Kwamared Ibrahim Ali, ya caccaki Baffa Babba Dan Agundi, bisa kalaman sa na rashin gaskiya.
Daga nan kungiyar ta bukaci Gwamna, Abdullahi Ganduje da ya gaggauta gudanar da bincike da kafa kwamitin da zai binciko ainihin adadin kudaden shiga da KAROTA ke samu a jihar.
Lamarin ya biyo bayan turka-turkar da ke akwai a tsakanin KAROTA da ‘Yan Adaidaita Sahu a jihar Kano.