Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya taya gwamna jihar Kano, Dr Abdullahi Ganduje murnar cika shekaru 72 a duniya.
Sakon taya murnar na shugaban na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu, ya fitar ranar Asabar a Abuja.
Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN ya rawaito cewa, shugaban ya bayyana Ganduje a matsayin ƙwararre mai gudanarwa wanda ya rubuta sabbin babi na ci gaba da zaman lafiya da tsaro a jihar Kano.
“Barka da ranar haihuwa da fatan alheri ga gwamna Ganduje. Ina yi muku fatan alheri da tsawon rai yayin da ku ke ci gaba da yi wa jiha da kasa hidima tare da sananniya da himma wajen samar da zaman lafiya da tsaro da ci gaba.
Ya kara da cewa “Jihar Kano na samun ci gaba a karkashin gwamnatin APC”. Inji Buhari.