Daruruwan fasinjojin jirgi na Azman Air da safiyar Talata sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matakin da aka dauka na dakatar da tashi daga Kano zuwa Legas da karfe 7:00 na safe.
DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa, ba a sanar da fasinjojin sokewar ba, har sai da ‘yan mintoci kadan da lokacin hawan jirgin ya yi.
Basu gamsu da sokewar ba, fusatattun fasinjojin suka tattaru a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, MAKIA, inda suka nufi ofishin jirgin saman Azman da ke kan titin Zariya, Kano domin bayyana kokensu.
Wasu daga cikin fasinjojin da suka gudanar da zanga-zangar sun koka kan yadda suke tafiya Legas, domin hada jiragen da za su je Landan, Masar, Dubai, Ghana da sauran wurare saboda rashin lafiya.
A halin da ake ciki, wani injiniya a kamfanin jirgin ya shaida wa wakilin DAILY NIGERIAN bisa sharadin sakaya sunansa cewa, ba zato ba tsammani na jirgin ya faru ne sakamakon wani gyara da ba a shirya yi ba aka kuma sauya lokacin tafiyar ta su.
A cewarsa, kamfanin ya lura da matsalar tsaro a cikin jirgin da aka shirya zai tashi da misalin karfe 4:00 na safe, inda ya kara da cewa, hukumar ba za ta iya yin komai ba, illa soke jirgin domin a gyara matsalar.
Sai dai ya ce an warware matsalar ta yadda wasu daga cikin fasinjojin suka amince a mayar da kudaden, yayin da wasu kuma suka zabi sauya jadawalin jiragen.