fidelitybank

Fasinjojin Azman Air a Kano sun yi zanga-zanga a kan sauke tashin su

Date:

Daruruwan fasinjojin jirgi na Azman Air da safiyar Talata sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matakin da aka dauka na dakatar da tashi daga Kano zuwa Legas da karfe 7:00 na safe.

DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa, ba a sanar da fasinjojin sokewar ba, har sai da ‘yan mintoci kadan da lokacin hawan jirgin ya yi.

Basu gamsu da sokewar ba, fusatattun fasinjojin suka tattaru a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, MAKIA, inda suka nufi ofishin jirgin saman Azman da ke kan titin Zariya, Kano domin bayyana kokensu.

Wasu daga cikin fasinjojin da suka gudanar da zanga-zangar sun koka kan yadda suke tafiya Legas, domin hada jiragen da za su je Landan, Masar, Dubai, Ghana da sauran wurare saboda rashin lafiya.

A halin da ake ciki, wani injiniya a kamfanin jirgin ya shaida wa wakilin DAILY NIGERIAN bisa sharadin sakaya sunansa cewa, ba zato ba tsammani na jirgin ya faru ne sakamakon wani gyara da ba a shirya yi ba aka kuma sauya lokacin tafiyar ta su.

A cewarsa, kamfanin ya lura da matsalar tsaro a cikin jirgin da aka shirya zai tashi da misalin karfe 4:00 na safe, inda ya kara da cewa, hukumar ba za ta iya yin komai ba, illa soke jirgin domin a gyara matsalar.

Sai dai ya ce an warware matsalar ta yadda wasu daga cikin fasinjojin suka amince a mayar da kudaden, yayin da wasu kuma suka zabi sauya jadawalin jiragen.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp