fidelitybank

Fasinjojin Azman Air a Kano sun yi zanga-zanga a kan sauke tashin su

Date:

Daruruwan fasinjojin jirgi na Azman Air da safiyar Talata sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matakin da aka dauka na dakatar da tashi daga Kano zuwa Legas da karfe 7:00 na safe.

DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa, ba a sanar da fasinjojin sokewar ba, har sai da ‘yan mintoci kadan da lokacin hawan jirgin ya yi.

Basu gamsu da sokewar ba, fusatattun fasinjojin suka tattaru a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, MAKIA, inda suka nufi ofishin jirgin saman Azman da ke kan titin Zariya, Kano domin bayyana kokensu.

Wasu daga cikin fasinjojin da suka gudanar da zanga-zangar sun koka kan yadda suke tafiya Legas, domin hada jiragen da za su je Landan, Masar, Dubai, Ghana da sauran wurare saboda rashin lafiya.

A halin da ake ciki, wani injiniya a kamfanin jirgin ya shaida wa wakilin DAILY NIGERIAN bisa sharadin sakaya sunansa cewa, ba zato ba tsammani na jirgin ya faru ne sakamakon wani gyara da ba a shirya yi ba aka kuma sauya lokacin tafiyar ta su.

A cewarsa, kamfanin ya lura da matsalar tsaro a cikin jirgin da aka shirya zai tashi da misalin karfe 4:00 na safe, inda ya kara da cewa, hukumar ba za ta iya yin komai ba, illa soke jirgin domin a gyara matsalar.

Sai dai ya ce an warware matsalar ta yadda wasu daga cikin fasinjojin suka amince a mayar da kudaden, yayin da wasu kuma suka zabi sauya jadawalin jiragen.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp