fidelitybank

Duk wanda ya yada labarin karya zai fuskanci daurin shekara 5 da tara – Saudiyya

Date:

Kasar Saudiyya ta gargaɗi al’ummarta cewa, duk wanda aka kama da yaɗa labaran kanzon Kurege a shafukan sada zumunta zai fuskantar ɗaurin shekara biyar tare da tara mai yawa.

Lamarin na zuwa ne bayan soke wani casu da aka yi a birnin Riyadh ya jawo rahotannin cewa an ci zarafin wasu mata da ke kan hanyar komawa gida.

Wasu daga cikin matan sun faɗa wa BBC fargabarsu ta bayyana abin da ya faru a shafukan zumunta bayan faruwarsa.

Sai dai shugaban sashen nishaɗantarwa na ƙasar ya yi fatali da iƙirarin nasu, har ma ya yi musu ba’a a dandalin Twitter.

Casun wanda aka tsara rukunin mawaƙa na K-Pop da Stray Kids za su gwangwaje a ranar 14 ga watan Janairu, an soke shi ne ana dab da farawa saboda rashin kyawun yanayi. Hakan ya jawo wasu ‘yan kallo sun sha wahala wajen komawa gida.

Daga nan ne kuma rahotanni suka fara ɓulla a shafukan zumunta cewa wasu yara mata sun ɓace da kuma yin gargaɗin lalata da su. Nan take aka fara ƙirƙirar maudu’ai a shafukan zumunta don nuna fargaba.

Babu wani tabbas game da haƙiƙanin abin da ya faru.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp