‘Yan wasan Falconets sun dawo Najeriya da sanyin safiyar ranar Alhamis, bayan fitar da su daga gasar cin kofin duniya ta mata ‘yan kasa da shekaru 20 ta 2022.
Sakatare Janar na Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF), Mohamed Sanusi da wakilin ministan matasa da wasanni, Toyin Ibitoye ne suka tarbi tawagar a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.
‘Yan wasan da jami’ansu sun fuskanci mummunan yanayi yayin da suka makale a filin jirgin saman Istanbul na tsawon sa’o’i 24 sakamakon gazawarsu na samun bizar wucewa.
An kuma yi jinkiri fiye da sa’o’i uku a Bogota, Colombia da sa’a daya a Panama.
Falconets ta sha kashi a hannun Netherlands da ci 2-1 a wasan daf da na kusa da karshe a Costa Rica 2022.
Tawagar Chris Danjuma ta lashe dukkan wasanninta na rukuni da Faransa da Koriya ta Kudu da kuma Canada a gasar.