Annobar cutar korona ta barke a fadar gwamnatin Najeriya, wadda a ke kira fadar shugaban kasa, kamar yadda a ka ce da yawa daga cikin hadiman shugaban kasa Muhammadu Buhari da manyan jami’an gwamnati sun kamu da cutar.
Sai dai gwamnatin Najeriyar ta shawarci ‘yan jaridu da su guji bayar da rahoton bullar cutar a fadar Villa.
Bincike ya nuna cewa baya ga babban sakatare a fadar gwamnatin, Tijjani Umar da mai taimakawa shugaban kasa (ADC), Yusuf Dodo; Babban jami’in tsaronsa (CSO), Aliyu Musa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, wadanda a ka tabbatar da sakamakonsu a cikin makon, Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed, shi ma ya kamu da cutar.
Wasu daga cikin jami’an da suka kamu da cutar ciki har da Mista Garba, kamar yadda majiya ta bayyana cewa an fitar da su daga taron majalisar zartaswa a ranar Laraba lokacin da sakamakon gwajin su na polymerase chain reaction (PCR) ya nuna hakan.
Garba Shehu, wanda ya tabbatar da cewa “sakamakon COVID-19 ne ya same shi,” a wani sakon rubutu da a ka rabawa manema labarai ranar Asabar, ya ce ba shi da “tabbacin” sauran gwaje-gwajen da a ka ambata a gare shi.
Ya kara da cewa ya riga ya samu lafiya, ya na mai cewa ya kammala atisayen nasa ne lokacin da wakilinmu ya kira waya, amma hakan na bukatar shaidar kimiyya domin ikirarin cewa ba ya dauke da kwayar cutar.
Sakon nasa ya na nuna cewa; “Ba ni da tabbaci game da lamuran da ku ka ambata, amma a bambance-bambancen COVID-19 sun shafe ni. Na ji lafiya daga farko, watakila saboda daya ya karbi duk jabs uku, kuma a yanzu, ina jin 100 bisa dari. Na gama atisayen gudu na tsawon awanni.
Kokarin jin martanin abokin aikin Malam Garba kuma mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Femi Adesina ya ci tura a kan lamarin, domin a kullum wayarsa na nuna cewa “waya ya ke yi” wato busy sawa a mala, idan an kira shi sau da yawa, shi ma bai mayar da martani ba, a gajeriyar sakon da a ka aika masa, bayan sa’o’i da yawa shi ma bai amsa ba.
A nasa bangaren, mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin zamani da sabbin kafafen yada labarai, Tolu Ogunlesi, ya ce ba zai iya cewa komai ba kan lamarin, kamar yadda ya mika wa wakilinmu ga wadanda ya bayyana a matsayin masu magana da yawun gwamnati.
Kokarin jin ta bakin ministan yada labarai, Mista Mohammed, shi ma bai haifar da wani sakamako mai kyau ba, domin sama da sa’o’i 24 ba a samu layin wayarsa ba, yayin da mai taimaka masa, Segun Adeyemi, bai amsa kiransa ba, kuma bai amsa wata gajeriyar sako da aka aika masa ba.
Sai dai wata majiya mai tushe ta tabbatar da cewa Lai Mohammed da sauran jami’an da abin ya shafa suna keɓe kuma suna samun kulawar likita.