Hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya (FAAN) ta nemi afuwar jinkirin da aka samu sakamakon ɗaukewar wutar lantarki a filin jirgin sama na Murtala Mohammed (MMIA), Legas.
Neman afuwar ya biyo bayan katsewar wutar lantarki da ta afku a filin jirgin da misalin karfe 11:15 na daren ranar Juma’a, inda fasinjoji da dama suka makale.
Mukaddashin Janar na FAAN, Faithful Hope-Ivbaze, ya nemi afuwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.
Sanarwar ta ce: “FAAN na neman afuwar fasinjoji da sauran masu amfani da filin jirgin da suka ga matsalar wutar lantarki ta wucin gadi a filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, da misalin karfe 23:15 a jiya, 1 ga Afrilu, 2022.
“Katsewar, wanda ya faru ne sakamakon ruwan sama da aka yi a jiya da ya zo da iska mai tsananin gaske da hadari, lamarin da ya faru ne na halitta, ya shafe mu, wanda hakan ya haifar da datsewar wutar lantarki na wucin gadi a D Wing na filin jirgin.