fidelitybank

EXPO 2020: Buhari ya tafi kasar hadadiyar Daular Larabawa

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja domin halartar bikin EXPO 2020 Dubai da ke Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Laraba.

Wata sanarwa dauke da sa hannun mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, wanda PlatinumPost ta samu, ta bayyana cewa, Buhari zai halarci taron bikin EXPO 2020 a Dubia.

Mista Adesina ya bayyana cewa, “EXPO 2020 Dubai, taren mai taken, “Wayar da kan al’umma, domin samun kyakyawar gobe”, ya samar da yanayin da Najeriya za ta shiga cikin ƙasashe sama da 190 domin kulla haɗin gwiwa na gaskiya da ma’ana “domin gina kyakkyawar makoma ga kowa da kowa. Bikin baje kolin zai sake baiwa tawagar Najeriya wata dama ta nuna gagarumin ci gaban da aka samu a fannin tattalin arziki a cikin shekaru shidan da suka gabata a matsayin ginshikin mayar da kasar nan muhimmiyar makoma ta zuba jari kai tsaye daga ketare”.

Shugaban kasar zai samu rakiyar ministocin harkokin waje, Geoffrey Onyeama, masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Otunba Adeniyi Adebayo, Kudi, kasafin kudi da tsare-tsare na kasa, Hajia Zainab Shamsuna Ahmed,  Tsaro, Manjo. Janar, Bashir Magashi (mai ritaya), Jirgin sama, Sanata Hadi Sirika, Noma da Raya Karkara, Dr. Mohammad Abubakar da dai sauran tawagar jami’an gwamnati.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp