Equatorial Guinea ta kai wasan zagaye na 16 na karshe a gasar cin kofin Afrika, bayan ta doke Saliyo da ci 1-0 sakamakon da ya fitar da Leone Stars.
Dan wasan tsakiya Pablo Ganet ne ya zura kwallo a ragar ‘yan wasan kafin a tafi hutun rabin lokaci.
Saliyo dai na bukatar maki ne, domin samun ci gaba, amma tsohon dan wasan gaba Kei Kamara ya farke a minti na 84 a bugun daga kai sai mai tsaron gida Jesus Owono.
Equatoguineans sun zo na biyu a rukunin E bayan Ivory Coast.
Yanzu dai kungiyar ta Juan Micha za ta kara da kungiyar da ta yi nasara a rukunin F ko wace daya daga cikin kasashen Gambia da Mali da Tunisia – ranar Laraba 26 ga watan Janairu.