fidelitybank

Duk wanda ya yada labarin karya zai fuskanci daurin shekara 5 da tara – Saudiyya

Date:

Kasar Saudiyya ta gargaɗi al’ummarta cewa, duk wanda aka kama da yaɗa labaran kanzon Kurege a shafukan sada zumunta zai fuskantar ɗaurin shekara biyar tare da tara mai yawa.

Lamarin na zuwa ne bayan soke wani casu da aka yi a birnin Riyadh ya jawo rahotannin cewa an ci zarafin wasu mata da ke kan hanyar komawa gida.

Wasu daga cikin matan sun faɗa wa BBC fargabarsu ta bayyana abin da ya faru a shafukan zumunta bayan faruwarsa.

Sai dai shugaban sashen nishaɗantarwa na ƙasar ya yi fatali da iƙirarin nasu, har ma ya yi musu ba’a a dandalin Twitter.

Casun wanda aka tsara rukunin mawaƙa na K-Pop da Stray Kids za su gwangwaje a ranar 14 ga watan Janairu, an soke shi ne ana dab da farawa saboda rashin kyawun yanayi. Hakan ya jawo wasu ‘yan kallo sun sha wahala wajen komawa gida.

Daga nan ne kuma rahotanni suka fara ɓulla a shafukan zumunta cewa wasu yara mata sun ɓace da kuma yin gargaɗin lalata da su. Nan take aka fara ƙirƙirar maudu’ai a shafukan zumunta don nuna fargaba.

Babu wani tabbas game da haƙiƙanin abin da ya faru.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp