fidelitybank

DSS: ‘Yan majalisa na cikin barazana

Date:

Hukumar tsaron farin Kaya ta (DSS) ta sanar da cewa ’yan majalisar dokoki na tarayya na fuskantar barazanar garkuwa domin neman kudin fansa ko kuma kisa.

DSS ta bayyana hakan ne a daidai lokacin da ’yan majalisar da sauran ’yan Najeriya ke shirye-shiryen tafiya hutu, domin bukukuwan karashen shekara.

Mai magana da yawun hukumar, Peter Afunanya ne ya sanar da hakan, ya na mai cewa, “Wadannan mutane suna cikin hadarin kisa da sacewa da garkuwa da su ko yi musu fashi tare da yi musu surkullen siyasa”. inji Peter Afunanya.

Karon farko ke nan da hukumar ta ambaci ’yan Majalisar Tarayya kai-tsaye a jerin mutanen da ke cikin hadarin garkuwa da su ko yi mu kisan gilla a Najeriya.

A baya hukumar kan yi wa ’yan majalisar kudin goro ne a cikin manyan mutane idan ta tashi fitar da gargadin jerin mutanen da ke cikin hadari ko barazanar tsaro.

A baya-bayan nan dai an ji wasu daga cikin ’yan Majalisar suna kokawa cewa lamarin matsalar tsaro a yankunan da su ke wakilta ta kai makura ta yadda su da kansu ba sa iya zuwa garuruwansu.

DSS ta bukaci ’yan majalisar da ’yan siyasa da ma’aikatan gwamanti da sauran jama’a cewa, su kasance masu lura da yanayin tsaro, domin kar Su fada cikin hadarin hari da miyagun makirce-makirce. Inji Aminya.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp