fidelitybank

DSS: ‘Yan majalisa na cikin barazana

Date:

Hukumar tsaron farin Kaya ta (DSS) ta sanar da cewa ’yan majalisar dokoki na tarayya na fuskantar barazanar garkuwa domin neman kudin fansa ko kuma kisa.

DSS ta bayyana hakan ne a daidai lokacin da ’yan majalisar da sauran ’yan Najeriya ke shirye-shiryen tafiya hutu, domin bukukuwan karashen shekara.

Mai magana da yawun hukumar, Peter Afunanya ne ya sanar da hakan, ya na mai cewa, “Wadannan mutane suna cikin hadarin kisa da sacewa da garkuwa da su ko yi musu fashi tare da yi musu surkullen siyasa”. inji Peter Afunanya.

Karon farko ke nan da hukumar ta ambaci ’yan Majalisar Tarayya kai-tsaye a jerin mutanen da ke cikin hadarin garkuwa da su ko yi mu kisan gilla a Najeriya.

A baya hukumar kan yi wa ’yan majalisar kudin goro ne a cikin manyan mutane idan ta tashi fitar da gargadin jerin mutanen da ke cikin hadari ko barazanar tsaro.

A baya-bayan nan dai an ji wasu daga cikin ’yan Majalisar suna kokawa cewa lamarin matsalar tsaro a yankunan da su ke wakilta ta kai makura ta yadda su da kansu ba sa iya zuwa garuruwansu.

DSS ta bukaci ’yan majalisar da ’yan siyasa da ma’aikatan gwamanti da sauran jama’a cewa, su kasance masu lura da yanayin tsaro, domin kar Su fada cikin hadarin hari da miyagun makirce-makirce. Inji Aminya.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp