Saudi Arabiya ta dawo da sanya takunkumin rufe baki da hanci a matsayin tilas ga ‘yan kasar da kuma kiyaye nisantar jama’a a gida da waje tun daga ranar Alhamis, a wani sabon yunkuri na dakile karuwar saurin kamuwa da cutar COVID-19.
Kamfanin dillancin labaran na kasar wanda Saudi gazzete ta wallafa ta rawaito cewa, ma’aikatar harkokin cikin gida ta Saudiyya a ranar Larabar nan ta ce, sabuwar shawarar za ta fara aiki ne daga karfe 7:00 na safe a ranar Alhamis 30 ga watan Disamba.
Majiyar ta yi nuni da cewa, a na bin dukkan matakai na ci gaba da tantance mutane daga kwararrun hukumomin kiwon lafiya ciki harda Masarautar, bisa ga ci gaban da aka samu na annobar cutar a kasar da ma duniya baki daya.
Majiyar ta yi kira ga kowa da kowa da su bi dukannin matakan kariya tare da jaddada mahimmancin rigakafin allurar Korona.
Majiyar ta bayyana cewa za a yi amfani da hanyoyin shari’a da yin hukunci kan masu karya doka.