Gwamantin jihar Kano ta ce ta na nazari a kan hukuncin da wata babbar kotu da ke birnin Abuja ta yanke na gwamnatin ta biya tsohon Sarki Kano Muhammadu Sanusi na II diyyar Naira miliyan 10 tare da neman gafararsa bisa korarsa daga jihar.
Kwamishinan shari’a na Kano Barista Musa Lawan ya shaida wa BBC cewa sai bayan gwamnati ta yi nazari kan hukuncin kotun sannan za ta san mataki na gaba da za ta dauka
“Mun sa lauyoyin mu su duba mana kundin shari’ar, domin mu yi nazari mu duba shi mu san ko za mu daukaka kara ko kuwa a’a, kundin tsarin mulki ya ba mu dama su duba su gani ko kotu ta yi hukuncin da ya dace”. Inji Barista Musa.
Kamfanin dillancin labaran na NAN, ya rawaito cewa mai shari’a Anjuli Chikere ta na cewa dokar majalisar sarakunan Kano ta 2019 wadda Gwamna Ganduje ya yi amfani da ita wajen korar tsohon sarkin daga jihar, bayan an sauke shi daga kan sarauta ta sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999.