Shugaban gidajen ajiya da gyaran hali na Najeriya, Halliru Nababa, ya ce akwai fursunoni ‘970 da suke yin karatun digiri a gidajen yari daban-daban na kasar’.
Jaridar DailyTrust ta rawaito cewa, shugaban ya bayyana haka ne a Abuja ranar Juma’a, inda ya ce fursunonin na karatun ne a jami’ar karatu daga nesa ta NOUN.
“Wadan nan daban suke daga cikin fursunonin da wadanda suka zana jarrabawar WAEC da NECO kuma suka samu sakamako mai kyau,” in ji shi.
Ya ce,”Lokacin za a ce dayuwar mutum ya zo karshe domin an kai shi gidan yari ta wuce, hukumar ta shirya, domin bai wa fursunoni horo gabanin mayar da su cikin al’umma, domin su zama wadanda al’umma za ta amfana da su a nan gaba”.