Darakta Janar na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa Yahaya Bello, Hafsat Abiola, ta shaida wa ‘yan Najeriya cewa, ita ce ke jagorantar yakin neman zaben Gwamna Yahaya Bello, domin ta yi nazari a kan mai neman tsayawa takara kuma ta ga irin halayen da ake bukata domin kai Najeriya inda ta dace.
Hafsat Abiola, diyar wanda ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 1993, Marigayi Cif MKO Abiola, ta ce, daya daga cikin kamanceceniya tsakanin mahaifinta mai taimakon jama’a da gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, shi ne yadda dukkansu suka ki samun ubangidan siyasa.
Ta ce hakan ne ya haddasa musgunawa da gwamnan ya fuskanta na bukatu daban-daban da kuma cece-kucen da ke tattare da gwamnatinsa.
Shugabar wanda ta yi magana a gidan talabijin na Arise TV a ranar Lahadi, ta bayyana kwarin gwiwar cewa, Bello zai ci tikitin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ba tare da la’akari da shiyyar shugaban kasa ba.