‘Yan sanda a jihar Kano sun gurfanar da wanda ake zargi da kashe yarinya ‘yar shekara 5, Hanifa Abubakar a gaba kotu
Yarinyar mai shekaru 5 malamin ta ne ya sace ta, aka kuma saka mata guba ta mutu, sannan aka yanke mata wuya, sannan aka binne ta a harabar makarantar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai ya ce, “Daga yanzu za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban babban kotun majistare 12 ta Gidan Murtala.”
SP Kiyawa ya bayyana cewa, za a tuhumi wadanda ake zargin da laifin hada baki satar mutane da boyewa da tsare wanda aka yi garkuwa da ita da kuma kisa.