Gwamnatin jihar Kano ta kwace lasisin dukkan makarantun firamare da sakandare masu zaman kansu da ke aiki a jihar.
Kano Focus ta rawaito cewa, sanarwar ta bayyana hakan ga manema labarai a yau ta bakin kwamishinan ilimi na jihar, Malam Sanusi Muhammad Kiru.
Kwamishinan ya ce, za a kafa kwamitin tantance dukannin makarantu masu zaman kansu a Kano.
Wannan dai na zuwa ne kwanaki kadan, bayan da wani ma’aikaranta mai zaman kanta ta, ya kashe wata yarinya ‘yar shekara biyar mai suna Haneefa Abubakar a Kano.