fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An yi wa shugaban kasar Burkina Faso juyin mulki

Date:

Jami’an tsaro sun kama shugaban kasar Burkina Faso, Roch Marc Christian Kabore.

A ranar Litinin din ne dai sojojin da suka yi kaurin suna suka bayyana cewa, gwamnatinsa ta gaza ba su goyon baya a yayin wani kazamin harin da aka kai musu.

Jaridar Dailypost ta rawaito cewa, an ji karar harbe-harbe tun a daren Lahadi a kusa da gidan Kabore, da ke birnin Ouagadougou, babban birnin kasar na Burkina Faso.

Rahotanni sun bayyana cewa, Kabore na tsare a wani sansanin soji, yayin da manyan wurare ke ganin an samu karin jami’an soji da motoci masu sulke.

Daruruwan sojoji rufe da fuska an jibge su a ginin kafafen yada labarai na gwamnati, RTB, wanda ke nuni da cewa, za a iya yada labarai nan ba da jimawa ba.

An yi imanin cewa, tattaunawar ta wargaje tsakanin masu yunkurin juyin mulkin da ministan tsaro, Janar Barthelemy Simpore.

Lamarin dai na nufin juyin mulkin da aka yi a Afirka, wanda ya fara a shekarar 2020, ya bazu zuwa shekarar 2022.

Masu fafutuka a Mali, karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita, sun tsige shugaba Ibrahim Boubacar Keita a watan Agustan 2018.

A watan Satumban 2021, manyan sojoji a Guinea, karkashin jagorancin Kanar Mamady Doumbouya, sun hambarar da shugaba Alpha Conde.

Sudan ta yi juyin mulki a watan Oktoban 2021 bayan yunkurin farko da bai yi nasara ba. Sojojin sun maido da ikon farar hula bayan wata yarjejeniya amma har yanzu suna cikin gwamnati.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuÆ™uru wajen daÆ™ile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta É—auki É—an wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen É—an wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe Æ´an Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp