Jami’an tsaro sun kama shugaban kasar Burkina Faso, Roch Marc Christian Kabore.
A ranar Litinin din ne dai sojojin da suka yi kaurin suna suka bayyana cewa, gwamnatinsa ta gaza ba su goyon baya a yayin wani kazamin harin da aka kai musu.
Jaridar Dailypost ta rawaito cewa, an ji karar harbe-harbe tun a daren Lahadi a kusa da gidan Kabore, da ke birnin Ouagadougou, babban birnin kasar na Burkina Faso.
Rahotanni sun bayyana cewa, Kabore na tsare a wani sansanin soji, yayin da manyan wurare ke ganin an samu karin jami’an soji da motoci masu sulke.
Daruruwan sojoji rufe da fuska an jibge su a ginin kafafen yada labarai na gwamnati, RTB, wanda ke nuni da cewa, za a iya yada labarai nan ba da jimawa ba.
An yi imanin cewa, tattaunawar ta wargaje tsakanin masu yunkurin juyin mulkin da ministan tsaro, Janar Barthelemy Simpore.
Lamarin dai na nufin juyin mulkin da aka yi a Afirka, wanda ya fara a shekarar 2020, ya bazu zuwa shekarar 2022.
Masu fafutuka a Mali, karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita, sun tsige shugaba Ibrahim Boubacar Keita a watan Agustan 2018.
A watan Satumban 2021, manyan sojoji a Guinea, karkashin jagorancin Kanar Mamady Doumbouya, sun hambarar da shugaba Alpha Conde.
Sudan ta yi juyin mulki a watan Oktoban 2021 bayan yunkurin farko da bai yi nasara ba. Sojojin sun maido da ikon farar hula bayan wata yarjejeniya amma har yanzu suna cikin gwamnati.