Mai horas da Najeriya na rikon kwarya, Augustine Eguavoen ya ajiye aiki a matsayin kocin rikon kwarya na tawagar kwallon kafar Najeriya.
Wannan ya biyo bayan rashin nasara da Super Eagles ta yi a hannun Tunisia da ci 1-0 a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2021 da suka fafata a zagaye na 16 a ranar Lahadi.
Eguavoen ya jagoranci Najeriya a gasar wanda ya fafata da Masar da Sudan da kuma Guinea-Bissau.
“Abin da zai biyo baya shi ne ni ne kociyan rikon kwarya, kuma Daraktan fasaha na hukumar kwallon kafa ta Najeriya (NFF). Yanzu kuma zan koma matsayi na kuma in ba da gudunmawa ta a NFF”. In ji Eguavoen bayan wasan.
Idan dai za a iya tunawa kasar Tunisia ta firgita Super Eagles ta Najeriya bayan fitar da su daga gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2021, inda suka zura kwallo a ragar ‘yan wasan bayan da aka dawo daga hutun rabin lokaci.
Kwallon da Youssef Msakni ya zura ta baiwa Carthage Eagles kwallo ta farko a wasan.