fidelitybank

Da Dumi-Dumi: An yi wa shugaban kasar Burkina Faso juyin mulki

Date:

Jami’an tsaro sun kama shugaban kasar Burkina Faso, Roch Marc Christian Kabore.

A ranar Litinin din ne dai sojojin da suka yi kaurin suna suka bayyana cewa, gwamnatinsa ta gaza ba su goyon baya a yayin wani kazamin harin da aka kai musu.

Jaridar Dailypost ta rawaito cewa, an ji karar harbe-harbe tun a daren Lahadi a kusa da gidan Kabore, da ke birnin Ouagadougou, babban birnin kasar na Burkina Faso.

Rahotanni sun bayyana cewa, Kabore na tsare a wani sansanin soji, yayin da manyan wurare ke ganin an samu karin jami’an soji da motoci masu sulke.

Daruruwan sojoji rufe da fuska an jibge su a ginin kafafen yada labarai na gwamnati, RTB, wanda ke nuni da cewa, za a iya yada labarai nan ba da jimawa ba.

An yi imanin cewa, tattaunawar ta wargaje tsakanin masu yunkurin juyin mulkin da ministan tsaro, Janar Barthelemy Simpore.

Lamarin dai na nufin juyin mulkin da aka yi a Afirka, wanda ya fara a shekarar 2020, ya bazu zuwa shekarar 2022.

Masu fafutuka a Mali, karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita, sun tsige shugaba Ibrahim Boubacar Keita a watan Agustan 2018.

A watan Satumban 2021, manyan sojoji a Guinea, karkashin jagorancin Kanar Mamady Doumbouya, sun hambarar da shugaba Alpha Conde.

Sudan ta yi juyin mulki a watan Oktoban 2021 bayan yunkurin farko da bai yi nasara ba. Sojojin sun maido da ikon farar hula bayan wata yarjejeniya amma har yanzu suna cikin gwamnati.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp