Rahotanni sun bayyana cewa, wasu da ake zargi sun jefa bama-bamai ne a sakatariyar jam’iyyar APC ta jihar Ribas da ke Fatakwal.
Lamarin ya faru ne a safiyar ranar Asabar, sa’o’i kadan da gudanar da zaben kananan hukumomi a jihar.
Kamar yadda wasu faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta na yanar gizo suka nuna, lamarin da ake zargin ’yan daba ne ya lalata babbar kofar shiga da kuma gidan tsaro na sakatariyar jam’iyyar APC, da kuma wasu sassan ginin da ke kusa da shi.
Shugaban kwamitin riko na babbar jam’iyyar adawa ta jihar, Cif Tony Okocha, ya tabbatar wa LEADERSHIP hakan.
Okocha ya zargi magoya bayan Gwamna Siminalayi Fubara da harin da aka kai a sakatariyar.
Okocha ya rubuta cewa: “Da sanyin safiyar Asabar, sojojin farar hula masu goyon bayan Fubara sun tayar da hayaki mai sa hawaye a ofishinmu.
“Yukuri na biyu na kona ta ya ci tura yayin da jami’an tsaron kofar suka kashe wutar da sauri.”