Gwamnatin tarayya ta mayar da martani kan rahoton, inda ta bayyana cewa akwai allurar wadda ta ke da karancin wa’adi wanda abu ne mai wuya ta iya kaiwa ga mutane ba tare da wa’adin ta ya kare ba.
Ministan lafiya, Dakta Osagie Ehanire ya bayyana cewa Najeriya ta yi amfani da allurar mai karancin wa’adi sama da milliyan goma kafin ta lalace, wanda hakan ya baiwa gwamnatin damar samun rarar kudi da su ka kai billiyan sha shida da digo hudu.
Ministan ya kuma bayyana dalilin da ya sanya Najeriya ta karbi allurar mai karacin wa’adi ya na mai cewa, saboda yawan al’umma da kasar ta ke da su da kuma saukin samu wanda hakan zai taimakawa Najeriyaa wajen rage kashe kudi.
Ya kuma tabbatar da cewa tuni hukumar NAFDAC ta kona allurar wanda ta riga ta lalace