fidelitybank

Copa Del Rey: Real Madrid za ta fuskanci Alcoyano

Date:

Real Madrid za ta yi tattaki zuwa Estadio El Collao da ke Alcoy a wasansu na farko a gasar, domin karawa da Alcoyano.

Shekaru biyu baya kenan, lokacin da kungiyar ta wulakanta kociyan kungiyar na wancan lokaci Zinedine Zidane da ‘yan wasansa bayan da suka sha kashi da ci 2-1.

Kungiyar wadda ta ke matakin aji na uku, wadda Alcoyano ta samu tikitin zuwa matakin na 32 a kakar wasa ta bana bayan da suka doke Levante da bugun daga kai sai mai tsaron gida, kuma wasan da suka yi ranar Juma’a a zagaye na gaba ya sa suka sake karawa da Madrid a gida.

Yanzu dai Carlo Ancelotti ke jagorantar Madrid, da alama Madrid ta kasance a matsayi mafi kyau fiye da yadda ta kasance a shekarar karshe da Zidane ya jagoranci kungiyar, bayan da ta samu gagarumin rinjaye a saman teburin La Liga kuma ta lashe wasanni biyar a gasar zakarun Turai na rukuni shida.

Barcelona za ta tunkari Linares Deportivo, wacce ta ke ajin matakin na uku, yayin da Atletico Madrid za ta fafata da Rayo Majadahonda.

Sevilla, wacce ke matsayi na biyu a gasar La Liga, za ta yi balaguro ne, domin karawa da Real Zaragoza wadda ta dauki kofin Copa sau shida, wadda ta fice daga gasar La Liga a 2012-13 kuma ta ci gaba da zama a rukunin Segunda.

Za a yi wasannin ne a tsakiyar mako daga 4-6 ga Janairu, in ji Hukumar FA (RFEF).

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp