fidelitybank

Copa Del Rey: Real Madrid za ta fuskanci Alcoyano

Date:

Real Madrid za ta yi tattaki zuwa Estadio El Collao da ke Alcoy a wasansu na farko a gasar, domin karawa da Alcoyano.

Shekaru biyu baya kenan, lokacin da kungiyar ta wulakanta kociyan kungiyar na wancan lokaci Zinedine Zidane da ‘yan wasansa bayan da suka sha kashi da ci 2-1.

Kungiyar wadda ta ke matakin aji na uku, wadda Alcoyano ta samu tikitin zuwa matakin na 32 a kakar wasa ta bana bayan da suka doke Levante da bugun daga kai sai mai tsaron gida, kuma wasan da suka yi ranar Juma’a a zagaye na gaba ya sa suka sake karawa da Madrid a gida.

Yanzu dai Carlo Ancelotti ke jagorantar Madrid, da alama Madrid ta kasance a matsayi mafi kyau fiye da yadda ta kasance a shekarar karshe da Zidane ya jagoranci kungiyar, bayan da ta samu gagarumin rinjaye a saman teburin La Liga kuma ta lashe wasanni biyar a gasar zakarun Turai na rukuni shida.

Barcelona za ta tunkari Linares Deportivo, wacce ta ke ajin matakin na uku, yayin da Atletico Madrid za ta fafata da Rayo Majadahonda.

Sevilla, wacce ke matsayi na biyu a gasar La Liga, za ta yi balaguro ne, domin karawa da Real Zaragoza wadda ta dauki kofin Copa sau shida, wadda ta fice daga gasar La Liga a 2012-13 kuma ta ci gaba da zama a rukunin Segunda.

Za a yi wasannin ne a tsakiyar mako daga 4-6 ga Janairu, in ji Hukumar FA (RFEF).

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci Æ™arya ne – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaÉ—awa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp