A karo na farko dan wasan kasar Denmark, Christian Eriksen, ya fara daukar horo tare da tsohuwar kungiyar sa Odense, tun bayan bugun zuciya da ta ritsa da shi a gasar cin kofin Euro 2020.
Eriksen ya fadi a lokacin bude gasar da kasar sa ta Denmark da Finland suka fafata a watan Yuni, kuma har ta kai sai da a ka yi masa aikin tiyata a zuciyar sa.
Dan wasan mai shekaru 29, an saka mai na’urar bugun zuciya (ICD), wanda ke nufin ba zai iya taka leda kungiyar sa ta Inter Milan a Seria A ba, saboda rashin cika bukatun samun motsa jiki.
Eriksen za a bar shi ya taka leda a wasu wasannin cikin gida a fadin Turai kuma, kamar yadda rahotanni daga BT a Denmark suka nuna, dan wasan ya kasance ya na amfani da wuraren horar da tsohon kungiyar sa ta OB, domin inganta lafiyarsa.