Gwamnatin Neja ta tabbatar da tsige sakataren hukumar sufuri ta Jihar, Abubakar Kolo, bisa zargin cin mutuncin kwamishiniyar sufuri, Hajiya Rahamatu Muhammad Yar’adua.
Shugaban ma’aikata, Hajiya Salamatu Abubakar ce ta bayyana hakan, a wata tattaunawa da ta yi da kwamitin harkokin sufuri na majalisar dokokin jihar a Minna ranar Alhamis.
An fara samun takun saka ne a yayin da a ke duba ayyukan kasafin kudin shekarar 2021 da kuma tantance kasafin kudin ma’aikatar sufuri ta 2022 da kwamitin majalisar kan harkokin sufuri ya yi a ranar Litinin.
Kwamishiniyar, Hajiya Ramatu Yaradua, ta yi zargin cewa sakataren ya ci mutuncinta a lokacin tantancewar.
Sai dai Abubakar ya ce a na ci gaba da gudanar da bincik,e domin bankado gaskiyar lamarin, inda ya kara da cewa mayar da aikin ba hukunci ba ne.
A jawabin sa babban sakataren ma’aikatar sufuri ta jihar, Alhaji Ibrahim Garba, ya ce, sakataren ya zagi kwamishinan ne a lokacin da ya shaida wa kwamitin cewa kwamishinan bai fadi gaskiya ba kan batun motocin safa da a ka siya wa hukumar ta NSTA.