Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama wasu ma’aikatan gwamnati guda Biyu, Muhammad Ahmad da Nelson Okoronkwo da kuma wani dalibi dan Najeriya a wanda ya ke karatu a kasar Japan, bisa nuna abin koyi na gaskiya da rikon amana da su ka yi.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, ya rawaito cewa, Tukur wanda shine mataimakin kwamandan a bangaren sha da fataucin miyagun kwayoyi, wanda a kwannan ya gano tare da kaddamarwa da hukumar Dala dubu 24,500 wanda wani dilan kwayoyi ya bayar a matsayin cinhanci, wanda kudaden na nufi ne a matsayin toshiya da za a yi da su kan hana binciken hodar Iblis wanda ta kai nauyin kilo 28, kuma kudin ta ya tasarwa biloyin Naira.
Shi kuwa Ikenna Nweke, wanda dalibi ne mai karatun digiri na Uku a jami’ar kasar Japan, kuma dan jihar Imo, ya gano wata jakar kudi da ke dauke da makudan kudade da wasu kayayyaki masu daraja, ya kuma mayar da su ga ‘yan sandan Japan, inda kuma ya ki amincewa da kashi 10 na kudaden da ya samu a lokacin da aka ba shi tukwicin.