Najeriya ta yi kasa da matsayi daya a cikin kididdigar da ake yi na yaki da cin hanci da rashawa (CPI) a shekarar 2021 da kungiyar Transparency International ta fitar a ranar Talata.
Najeriya ta sami maki 24 cikin maki 100 a cikin kididdigar na 2021, wanda aka bayyana a shafin TI na Twitter @TranperencITng.
Wannan dai ita ce shekara ta biyu a jere a Najeriya da koma bayanta a kimar TI ta CPI, inda makin kasar ya ragu daga 26 a shekarar 2019 zuwa 25 a kimar shekarar 2020, kuma ya kara zuwa 24 a sabon jadawalin na shekarar 2021.
Najeriya ta rike matsayi na 149 a cikin kasashe 180 da aka gudanar da bincike a kan lamarin, wanda hakan ya sa ta zama kasa ta biyu a yammacin Afirka da aka fi cin hanci da rashawa.
Matsayin na iya zama manuniya cewa, cin hanci da rashawa ya yi tsanani a cikin shekaru.