fidelitybank

A gaggauta gudanar da binciken turmutsutsun da aka yi a wasan Kamaru – Paul Biya

Date:

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan abin da ya janyo aka yi turmutsutsun da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum takwas a wajen filin wasa a babban birnin kasar Yaoundé kafin wani wasana gasar cin kofin Afirka.

Wata sanarwa da gwamnati ta fitar ta ce, binciken zai sa a gano abin da ya haddasa lamarin.

Turmutsutsun ya faru ne a lokacin da magoya baya suka yi kokarin kutsawa cikin filin wasan Olembe kafin karawar Kamaru da Komoros (Comoros) .

Bayan wadanda suka rasa ransu, wasu mutum talatin kuma sun ji rauni.

Ba a dai tsara cewa, mutane da yawa za su shiga kallon wasan ba, saboda matakan kariya na cutar korona, amma wadanda suka ga abin da ya faru sun ce tarin magoya baya sun je domin shiga cikin filin.

Hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf), wadda ta shirya gasar ita ma ta kaddamar da nata binciken.

Kamaru wadda ta yi nasarar zuwa wasan dab da na kusa da karshe bayan ta doke Komoros da ci 2-1, a wasan, yanzu za ta kara da Gambia, wadda ita kuma ta ci Guinea 1-0.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp