fidelitybank

Buhari ya yabawa Ganduje a kan addu’o’in zaman lafiya

Date:

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yabawa gwamnatin jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, bisa shirya taron yi wa kasa addu’a.

Shugaba Buhari wanda ya samu wakilcin wakilcin ministan ma’aikatar ayyukan gona, Alhaji Mustapha Baba Shahuri.

Ya ce, an shirya taron a dai-dai lokacin da ya da ce, inda ya ce dama addu’a ce kadai hanyar maganin matsalolin kasar nan.

ya bayyana hakan ne yayin taron yiwa Kasa addu’a wadanda Gwamnatin Jihar Kano ta Shirya da nufin Samun saukin Matsalolin tsaro da ake fuskanta a Wasu jihohin Kasar nan.

A jawabinsa gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce, an shirya taron ne domin kaskantar da kai ga Allah tare da rikonsa ya kawowa Najeriya saukin matsalolin da a ke fuskanta.

Ya kuma bada tabbacin duk shekara gwamnatin za ta rikka shirya taron kamar yadda shugaban kasa ya bukata, tare da yin roko ga Sheikh Dahiru Usman Bauchi da ya amince da bukatar gwamnatin Kano na gudanar da mauludin Shehu Ibrahim Inyas na kasa a Kano.

Gwamna Ganduje ya godewa duk mahalatta taron musamman Khalifan Tijjaniya na Duniya Sheikh Sidi Ali Bil Arabi da ‘yan tawagar sa bisa halartar Kano da su kai, domin yi wa Najeriya addu’o’in samun zaman lafiya.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana lokacin taron Addu,a da gwamnatin Kano ta shirya a filin wasa na Sani Abacha da ke nan kano.

Da ya ke nasa jawabin sa, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, bayan ya yabawa gwamna Ganduje,ya kuma bada tabbacin za su kawo Mauludin Sheikh Ibrahim Inyas na wannan shekarar Kano kamar yadda Gwamnan ya roka.

Sheikh Dahiru Bauchi ya kuma yabawa shugaban kasa, Muhammadu Buhari, kan yadda ya ke kokari wajen inganta tsaro a kasar nan.

 

 

 

 

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp