fidelitybank

Buhari ya yabawa Ganduje a kan addu’o’in zaman lafiya

Date:

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yabawa gwamnatin jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, bisa shirya taron yi wa kasa addu’a.

Shugaba Buhari wanda ya samu wakilcin wakilcin ministan ma’aikatar ayyukan gona, Alhaji Mustapha Baba Shahuri.

Ya ce, an shirya taron a dai-dai lokacin da ya da ce, inda ya ce dama addu’a ce kadai hanyar maganin matsalolin kasar nan.

ya bayyana hakan ne yayin taron yiwa Kasa addu’a wadanda Gwamnatin Jihar Kano ta Shirya da nufin Samun saukin Matsalolin tsaro da ake fuskanta a Wasu jihohin Kasar nan.

A jawabinsa gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce, an shirya taron ne domin kaskantar da kai ga Allah tare da rikonsa ya kawowa Najeriya saukin matsalolin da a ke fuskanta.

Ya kuma bada tabbacin duk shekara gwamnatin za ta rikka shirya taron kamar yadda shugaban kasa ya bukata, tare da yin roko ga Sheikh Dahiru Usman Bauchi da ya amince da bukatar gwamnatin Kano na gudanar da mauludin Shehu Ibrahim Inyas na kasa a Kano.

Gwamna Ganduje ya godewa duk mahalatta taron musamman Khalifan Tijjaniya na Duniya Sheikh Sidi Ali Bil Arabi da ‘yan tawagar sa bisa halartar Kano da su kai, domin yi wa Najeriya addu’o’in samun zaman lafiya.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana lokacin taron Addu,a da gwamnatin Kano ta shirya a filin wasa na Sani Abacha da ke nan kano.

Da ya ke nasa jawabin sa, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, bayan ya yabawa gwamna Ganduje,ya kuma bada tabbacin za su kawo Mauludin Sheikh Ibrahim Inyas na wannan shekarar Kano kamar yadda Gwamnan ya roka.

Sheikh Dahiru Bauchi ya kuma yabawa shugaban kasa, Muhammadu Buhari, kan yadda ya ke kokari wajen inganta tsaro a kasar nan.

 

 

 

 

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp