fidelitybank

Abdullahi Abbas ya zama sabon shugaban majalisar gamayyar jam’iyun siyasa

Date:

Majalisar gamayyar jam’iyun siyasa ta kasa ta zabi, shugaban jam’iyar APC, Abdullahi Abbas a matsayin shugaban majalisar reshen jihar Kano.

Da ya ke rantsar da sabbin shugabannin wakilin majalisar na kasa wanda ya jagoranci gabatar da zaben, Nasir Sidi Ali, ya ce, dukkan shugabannin an zabe su ne bayan cika dukkan ka’idojin majalisar.

Ya ce,”Dan takarar jam’iyar APC Abdullahi Abbas shi ne ya yi nasara da kuri’u 13 daga cikin kuri’u 14 da a ka kada a zaben”. In ji Nasir Sidi

A tattaunawar sa da manema labari bayan an rantsar da shi, Abdullahi Abbas ya ce, gamayyar jam’iyun karkashin jagorancinsa zai yi duk mai yuwa, domin ci gaban dimokuradaiyya.

Ya kuma ce,”Duk da cewa kowannen su ya na da jam’iyar sa, amma hakan ba zai hana mu ci gaba da aiki tare da sub a, domin ci gaban majalisar da ma jihar Kano baki da ya”. A cewar Abdullahi Abbas.

An dai zabi Abdullahi abbas na jam’iyar APC a matsayin shugaba yayin da Isa Nuhu Isa ya kasance a matsayin matemakin shugaba sai Nuhu Idris Adam na jam’iyar APM a matsayin sakatare da Abdullahi A Sharif na jam’iyar AAC a matsayin matemakin sakatare.

Sauran shugabannin sun hada da: Ado Muhammad na jami’iyar NRM a matsayin ma’aji da Bello Ado Usaini a matsayin sakataren shirye-shirye, sai sakataren kudi wanda a ka zabi Nasiru Aliko na jami’iyar ADP da Ibrahim Muhammad na jami’iyar APP a matsayin sakataren yada labarai na majalisar da kuma Salisu Umar na jami’iyar YPP a matsayin mai bada shawara a harkokin shari’a.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp