Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tattauna da ‘yan wasan Super Eagles, gabanin wasansu na zagaye na biyu da kasar Tunisia a gasar cin kofin nahiyar Afrika da aka shirya gudanarwa a daren yau Lahadi.
Da yake magana ta hanyar bidiyo daga fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja, shugaban ya tattauna da Koci Augustine Eguavoen, da kyaftin Ahmed Musa da Amaju Pinnick, shugaban hukumar kwallon kafa ta Najeriya (NFF), da sauran su.
Shugaba Buhari da ya ambaci sunayen biyu daga cikin ‘yan wasan, Kelechi Iheanacho da Moses Simon, ya bukaci Super Eagles da su ci gaba da faranta wa ‘yan Najeriya rai, ba wai kawai ta lashe wasan zagaye na biyu ba, amma a karshe su dauke kofin.
Shugaban ya ce: “Ku na yi wa Najeriya alfahari. Ku na cin nasara. Da fatan za a ci gaba da yin nasara. Gwamnatin Tarayya ta na ba ku goyon baya, kuma na ce na gode wa dukkan ma’aikata da ’yan wasa..Da fatan za a ci gaba da yi wa kasa alfahari.” In ji Buhari.
Shugaba Buhari, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina, ya fitar, ya yaba wa ministan wasanni da ci gaban matasa, Sunday Dare bisa kyakkyawan aikin da yake yi.
Da yake mayar da martani, Koci Eguavoen ya ce; “Mun ji dadin yadda mai girma shugaban kasa Buhari ya tattauna da mu a safiyar yau. A madadin ‘yan wasa da ma’aikatan kungiyar, ina so in ce mun gode sosai”. A cewar Eguavoen.