Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma jigo a jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Sanata Ahmed Sani Yarima, ya sake ayyana aniyyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasa a zaben 2023.
Sanata Yarima wanda tun a shekara ta 2007 ya fara fitowa takarar shugabancin kasa, ya yi watsi da tsarin karba-karba a zaman abin da ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar duk da cewar, a na ganin lokaci ne da ya kamata yankin Kudancin kasar ya fitar da shugaban kasa na gaba.
BBC ta rawaito cewa ya bayyana aniyar sa ta neman shugababancin kasar da kuma matsayinsa game da rikicin shugabancin da jam’iyyar tasa ke fama da shi a jiharsa ta zamfara.