fidelitybank

Buhari ya umarci Super Eagles su kawo kofin AFCON Najeriya

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tattauna da ‘yan wasan Super Eagles, gabanin wasansu na zagaye na biyu da kasar Tunisia a gasar cin kofin nahiyar Afrika da aka shirya gudanarwa a daren yau Lahadi.

Da yake magana ta hanyar bidiyo daga fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja, shugaban ya tattauna da Koci Augustine Eguavoen, da kyaftin Ahmed Musa da Amaju Pinnick, shugaban hukumar kwallon kafa ta Najeriya (NFF), da sauran su.

Shugaba Buhari da ya ambaci sunayen biyu daga cikin ‘yan wasan, Kelechi Iheanacho da Moses Simon, ya bukaci Super Eagles da su ci gaba da faranta wa ‘yan Najeriya rai, ba wai kawai ta lashe wasan zagaye na biyu ba, amma a karshe su dauke kofin.

Shugaban ya ce: “Ku na yi wa Najeriya alfahari. Ku na cin nasara. Da fatan za a ci gaba da yin nasara. Gwamnatin Tarayya ta na ba ku goyon baya, kuma na ce na gode wa dukkan ma’aikata da ’yan wasa..Da fatan za a ci gaba da yi wa kasa alfahari.” In ji Buhari.

Shugaba Buhari, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina, ya fitar, ya yaba wa ministan wasanni da ci gaban matasa, Sunday Dare bisa kyakkyawan aikin da yake yi.

Da yake mayar da martani, Koci Eguavoen ya ce; “Mun ji dadin yadda mai girma shugaban kasa Buhari ya tattauna da mu a safiyar yau. A madadin ‘yan wasa da ma’aikatan kungiyar, ina so in ce mun gode sosai”. A cewar Eguavoen.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...
X whatsapp