fidelitybank

Buhari ya umarci Super Eagles su kawo kofin AFCON Najeriya

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tattauna da ‘yan wasan Super Eagles, gabanin wasansu na zagaye na biyu da kasar Tunisia a gasar cin kofin nahiyar Afrika da aka shirya gudanarwa a daren yau Lahadi.

Da yake magana ta hanyar bidiyo daga fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja, shugaban ya tattauna da Koci Augustine Eguavoen, da kyaftin Ahmed Musa da Amaju Pinnick, shugaban hukumar kwallon kafa ta Najeriya (NFF), da sauran su.

Shugaba Buhari da ya ambaci sunayen biyu daga cikin ‘yan wasan, Kelechi Iheanacho da Moses Simon, ya bukaci Super Eagles da su ci gaba da faranta wa ‘yan Najeriya rai, ba wai kawai ta lashe wasan zagaye na biyu ba, amma a karshe su dauke kofin.

Shugaban ya ce: “Ku na yi wa Najeriya alfahari. Ku na cin nasara. Da fatan za a ci gaba da yin nasara. Gwamnatin Tarayya ta na ba ku goyon baya, kuma na ce na gode wa dukkan ma’aikata da ’yan wasa..Da fatan za a ci gaba da yi wa kasa alfahari.” In ji Buhari.

Shugaba Buhari, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Femi Adesina, ya fitar, ya yaba wa ministan wasanni da ci gaban matasa, Sunday Dare bisa kyakkyawan aikin da yake yi.

Da yake mayar da martani, Koci Eguavoen ya ce; “Mun ji dadin yadda mai girma shugaban kasa Buhari ya tattauna da mu a safiyar yau. A madadin ‘yan wasa da ma’aikatan kungiyar, ina so in ce mun gode sosai”. A cewar Eguavoen.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp