Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya wata ganawar sirri da tsohon shugaban kasa, Dr Goodluck Jonathan a fadar shugaban kasa dake Abuja a ranar Alhamis.
Sai dai kuma kawo wannan lokacin ba a iya bayyana ganawar ta su da tsohon shugaban kasar da a ka yi da misalin karfe 3 na rana ba.
Sai dai Jonathan na zuwa fadar shugaban kasa akai-akai, domin yi wa shugaban kasa bayanin ayyukansa a matsayinsa na mai wanzar da zaman lafiya na musamman na kungiyar ECOWAS a Mali.
Karin bayani zai zo mu a nan gaba dangane da tattaunawar shugaba Buhari da Goodluck.