fidelitybank

Ballon d’Or: Ronaldo ya mayar da martani mai zafi a kan kyautar

Date:

Cristiano Ronaldo ya zargi editan kwallon kafa na Faransa da yin karya bayan ya ce burin dan kasar Portugal shi ne ya yi ritaya da karin kyautar Ballon d’Or fiye da Lionel Messi.

Mai shirya Ballon d’Or Pascal Ferre ne ya yi wannan ikirarin ga jaridar New York Times.

A ranar Litinin ne Messi na Paris St-Germain ya lashe kyautar Ballon d’Or karo na bakwai, yayin da Ronaldo wanda ya lashe sau biyar ya zo na shida.

Ronaldo ya ce “A ko da yaushe ina yin nasara ga kaina da kuma kungiyoyin da na ke wakilta. Na yi nasara ga kaina da kuma wadanda suke so na, ba na cin nasara a kan wani.”

A ranar Juma’a, Ferre ya shaida wa jaridar New York Times cewa: “Ronaldo ya na da buri daya kacal, kuma shi ne ya yi ritaya da karin Ballon d’Or fiye da Messi, kuma na san hakan saboda ya fada min”.

Ronaldo ya mayar da martani a shafukan sada zumunta inda ya ce, “Pascal Ferre ya yi karya, ya yi amfani da sunana wajen tallata kansa da kuma tallata littafin da ya ke yi wa aiki. Ba abin yarda ba ne cewa mutumin da ke da alhakin bayar da irin wannan babbar kyautar zai iya yin karya ta wannan hanyar, ba tare da mutunta wanda ya taba mutunta kwallon kafa ta Faransa Football da Ballon d’Or ba. Babban burina a rayuwata shi ne na lashe kofunan kasa da kasa a kungiyoyin da na ke wakilta da kuma ‘yan wasan kasa a kasata. Babban burina a rayuwata shine in bar sunana a rubuce a cikin haruffan zinare a tarihin kwallon kafa na duniya.” Inji Ronaldo.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp