fidelitybank

Ballon d’Or: Messi ya lashe kyautar sau 7

Date:

Dan wasan gaba na Paris St-Germain da kasar Argentina, Lionel Messi ya lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na duniya wato Ballon d’Or na bana a karo na bakwai.

Messi, mai shekaru 34, ya taimaka wa kasarsa ta lashe kofin Copa America, wanda ya zama lambar karramawa ta farko a duniya, kuma ya ci kwallaye 40 a kakar shekarar 2021 da 28 a Barcelona, ​​Hudu a Paris St-Germain da Takwas a Argentina.

Dan wasan gaba na Bayern Munich da kasar Poland Robert Lewandowski ne ya zo na Biyu, dan wasan tsakiya na Chelsea da Italiya Jorginho ya zo na Uku sai dan wasan gaban Real Madrid na Faransa Karim Benzema ya zo na Hudu.

‘Yan jarida 180 ne suka kada kuri’ar Ballon d’Or daga ko’ina cikin duniya, duk da cewa ba a samu kyautar ba a shekarar 2020 saboda cutar Corona.

Ko dai Messi ko Cristiano Ronaldo sun lashe kyautar har sau Biyar ne a duk shekara daga 2008 zuwa 2019, baya ga 2018 da dan wasan tsakiya na Croatia, Luka Modric ya lashes au Daya.

Messi ya riga ya lashe kofin fiye da kowane dan wasa kuma nasararsa ta Bakwai ta zo ne bayan ya lashe a shekarar 2009, 2010, 2011, 2012, 2015 da kuma 2019.

Lewandowski ya zura kwallaye 53 a dukkan gasa a shekarar 2021 a Bayern kuma an ba shi kyautar gwarzon dan wasan gaba, sabuwar kyautar da aka sanar sa’o’i kadan kafin fara bikin.

Gianluigi Donnarumma na Paris St-Germain, wanda ya taimakawa Italiya lashe gasar Euro 2020, ya lashe kyautar Yashin Trophy a matsayin mafi kyawun mai tsaron gida, yayin da Chelsea ta lashe gasar zakarun Turai ta lashe kyautar kungiya mafi kyawun shekara.

Dan wasan tsakiya na Barcelona Pedri, mai shekaru 19, ya lashe Kopa Trophy a matsayin gwarzon dan wasa mai shekaru kasa da 21, inda ‘yan wasan Ingila Jude Bellingham, Mason Greenwood da Bukayo Saka suka zo na Biyu da na Biyar da na Shida.

‘Yan wasa 14 daga cikin 30 da aka zaba a matsayin Ballon d’Or a halin yanzu suna buga gasar Premier.

 

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp