fidelitybank

Ballon d’Or: Messi ya lashe kyautar sau 7

Date:

Dan wasan gaba na Paris St-Germain da kasar Argentina, Lionel Messi ya lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafa na duniya wato Ballon d’Or na bana a karo na bakwai.

Messi, mai shekaru 34, ya taimaka wa kasarsa ta lashe kofin Copa America, wanda ya zama lambar karramawa ta farko a duniya, kuma ya ci kwallaye 40 a kakar shekarar 2021 da 28 a Barcelona, ​​Hudu a Paris St-Germain da Takwas a Argentina.

Dan wasan gaba na Bayern Munich da kasar Poland Robert Lewandowski ne ya zo na Biyu, dan wasan tsakiya na Chelsea da Italiya Jorginho ya zo na Uku sai dan wasan gaban Real Madrid na Faransa Karim Benzema ya zo na Hudu.

‘Yan jarida 180 ne suka kada kuri’ar Ballon d’Or daga ko’ina cikin duniya, duk da cewa ba a samu kyautar ba a shekarar 2020 saboda cutar Corona.

Ko dai Messi ko Cristiano Ronaldo sun lashe kyautar har sau Biyar ne a duk shekara daga 2008 zuwa 2019, baya ga 2018 da dan wasan tsakiya na Croatia, Luka Modric ya lashes au Daya.

Messi ya riga ya lashe kofin fiye da kowane dan wasa kuma nasararsa ta Bakwai ta zo ne bayan ya lashe a shekarar 2009, 2010, 2011, 2012, 2015 da kuma 2019.

Lewandowski ya zura kwallaye 53 a dukkan gasa a shekarar 2021 a Bayern kuma an ba shi kyautar gwarzon dan wasan gaba, sabuwar kyautar da aka sanar sa’o’i kadan kafin fara bikin.

Gianluigi Donnarumma na Paris St-Germain, wanda ya taimakawa Italiya lashe gasar Euro 2020, ya lashe kyautar Yashin Trophy a matsayin mafi kyawun mai tsaron gida, yayin da Chelsea ta lashe gasar zakarun Turai ta lashe kyautar kungiya mafi kyawun shekara.

Dan wasan tsakiya na Barcelona Pedri, mai shekaru 19, ya lashe Kopa Trophy a matsayin gwarzon dan wasa mai shekaru kasa da 21, inda ‘yan wasan Ingila Jude Bellingham, Mason Greenwood da Bukayo Saka suka zo na Biyu da na Biyar da na Shida.

‘Yan wasa 14 daga cikin 30 da aka zaba a matsayin Ballon d’Or a halin yanzu suna buga gasar Premier.

 

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp