Gwamnatin jihar Jigawa ta ayyana ranar Juma’a 26 ga watan Agusta, 2022 a matsayin ranar da babu aiki domin tunawa da cika shekaru 31 da kafa jihar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Hussaini Ali Kila ya sanya wa hannu ga jaridar DAILY POST.
A cewar sanarwar, Gwamna Badaru Abubakar ya taya ma’aikatan gwamnati da daukacin al’ummar jihar murnar zagayowar ranar.
Sanarwar ta kuma bukaci jama’a da su yi addu’a ga jihar da kasa baki daya yayin gudanar da bukukuwan ranar.
Ya shawarci ma’aikatan gwamnati da daukacin al’ummar jihar da su yi amfani da hutun kwana daya wajen gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya ba su yanayi mai kyau, da zaman lafiya tare da yi masa addu’ar Allah ya kawo mana dauki domin ceto al’ummar kasar daga kalubalen tsaro da ke addabarsu.
An kafa jihar Jigawa daga tsohuwar jihar Kano a ranar Talata 27 ga watan Agusta 1991 da shugaban mulkin soja na lokacin, Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya kafa.