fidelitybank

Babu maganar sulhu ni da Ganduje – Kwankwaso

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya musanta batun tattaunawar sulhu da a ka ce ya na yi da Gwamnan Jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Aminiya ta rawaito cewa, Kwankwaso ya bayyana haka ne cikin wata hira ta musamman da a ka yi da shi a gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, inda ya ce. ya ji dadin ziyarar ta’aziyyar da Gwamnan ya kai masa ta rasuwar kaninsa.

Sai dai ya kore yiwuwar bawa Ganduje damar samun wani matsayi ko mukami idan damar hakan ta samu ta bangarensa.

Ya ce “A yanzu dai ka san ba a jam’iyya daya mu ke ba, domin haka ina ganin babu ma bukatar yin wannan tambaya, domin haka ko da dama ta samu akwai mutanen da suka cancanta cikin wadanda na ke tare da su”.

A makon da ya wuce Kwankwaso ya musanta rade-radin da a ke na cewar ya na shirin ficewa daga jam’iyyar PDP tare da shirin sauya sheka zuwa APC, wanda hakan ya zama batun tattaunawa na tsawon lokaci a kafafen watsa labarai.

Rikicin Kwankwaso da Ganduje ya yi tsamari tun bayan 2015 bayan Gwamnan Kano na yanzu ya dare kan kujerar mulkin Jihar.

Sai dai a baya-bayan Ganduje ya nuna cewar akwai yiwuwar yin sulhu da tsohon uban gidan nasa a siyasa, wanda ya ce tun asali wasu ne suka shiga tsakaninsu.

Gwamna Ganduje na ci gaba da fuskantar rikicin cikin gida a jam’iyyarsu ta APC tsakaninsa da tsagin tawagar tsohon Gwamna kuma Sanatan Kano ta tsakiya a yanzu, Malam Ibrahim Shekarau.

Wanda a ke rikicin shugabancin jam’iyya tsakanin, Abdullahi Abbas da Haruna Abdullahi Zago.

 

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp