Yayin da a ka koma makarantu a faɗin Najeriya a ranar Litinin, wasu iyayen yara a jihar Zamfara sun koka a kan rashin buɗe makarantun su.
Mazauna yankin sun ce rashin komawa makarantun ‘ya’yansu a safiyar yau, alama ce da ke nuna cewa dubban ‘ya’yan talakawa a jihar za su ci gaba da zaman gida tsawon zangon karatu na biyu ke nan.
Gwamnatin Zamfara dai ta rufe makarantun jihar ne a farkon watan Satumba, bayan sace gomman ɗalibai daga Sakandiren Ƙaya a cikin ƙaramar hukumar Muradun da yammacin ranar wata Laraba.
Wani mahaifi ya shaida wa BBC cewa suna tsaka mai wuya; ”Mu na kira ga gwamnatin jihar Zamfara ta duba girman Allah ta bude mana makarantun yara, wannan matsalar tsaro wadda ita ce a ka ce ta janyo rufe makarantun ba wai Zamfara kadai ta shafa ba, shin don me a nan za a mayar tamkar nan ne gidan matsalar”.
An yi zango guda yara na zaman gida, yanzu duk inda za a koma makaranta ban da namu ‘ya’yan. Kowancan Term guda da aka yi wasu daga cikin mutanenmu da sun san ba za a koma makarantar ba da tuni sun dauki mataki,” in ji shi.
An dai rufe makarantu tun watan Agustan bara, watanni biyar kenan, kuma babu wata magana guda har ya zuwa yanzu na bude makarantun.