fidelitybank

Ba za a iya samun asara a yakin makan kare dangi ba – Kasashen Ketare

Date:

Kasashen China da Rasha da Birtaniya da Amurka da Faransa sun amince cewa ya kamata a kaucewa ci gaba da yaduwar makaman kare dangi da kuma yakin nukiliya.

A cewar sanarwar hadin gwiwa da kasashe biyar masu karfin makamin nukiliyar da fadar Kremlin ta wallafa a ranar Litinin.

Ta ce kasashen biyar wadanda su ne mambobi na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, sun dauki alhakinsu na farko na kaucewa yaki tsakanin kasashen da ke amfani da nukiliya da kuma rage hadarurruka, yayin da su ke da niyyar hada kai da dukkan kasashen wajen domin samar da yanayi na tsaro.

“Mun ayyana cewa ba za a iya samun nasara a yakin makaman kare dangi ba na nukiliya, bai kamata a fara shi ba,” in ji sanarwar da yaren Rasha.

“Kamar yadda amfani da makaman nukiliya zai haifar da sakamako mai nisa, muna kuma tabbatar da cewa makaman nukiliya – muddun akwai su – ya kamata su yi aiki da manufofin kariya, da hana wuce gona da iri da rigakafin yaki.”

“Ita ma kasar Faransa ta fitar da sanarwar, inda ta jaddada cewa kasashe biyar din sun jaddada aniyarsu na sarrafa makaman kare dangi da kuma daura damara. Za su ci gaba da bin hanyoyin da za su bi wajen sarrafa makaman kare dangi da na nukiliya”, in ji shi.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da a ke samun karuwar tashe-tashen hankula na siyasa a tsakanin Rasha da kasashen yammacin Turai, saboda damuwar da Rasha ke yi game da girke sojojinta a kusa da makwabciyarta Ukraine. Moscow ta ce za ta iya zagayawa da sojojinta zuwa yankinta kamar yadda ta ga ya dace.

 

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp