fidelitybank

Ba za a iya samun asara a yakin makan kare dangi ba – Kasashen Ketare

Date:

Kasashen China da Rasha da Birtaniya da Amurka da Faransa sun amince cewa ya kamata a kaucewa ci gaba da yaduwar makaman kare dangi da kuma yakin nukiliya.

A cewar sanarwar hadin gwiwa da kasashe biyar masu karfin makamin nukiliyar da fadar Kremlin ta wallafa a ranar Litinin.

Ta ce kasashen biyar wadanda su ne mambobi na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, sun dauki alhakinsu na farko na kaucewa yaki tsakanin kasashen da ke amfani da nukiliya da kuma rage hadarurruka, yayin da su ke da niyyar hada kai da dukkan kasashen wajen domin samar da yanayi na tsaro.

“Mun ayyana cewa ba za a iya samun nasara a yakin makaman kare dangi ba na nukiliya, bai kamata a fara shi ba,” in ji sanarwar da yaren Rasha.

“Kamar yadda amfani da makaman nukiliya zai haifar da sakamako mai nisa, muna kuma tabbatar da cewa makaman nukiliya – muddun akwai su – ya kamata su yi aiki da manufofin kariya, da hana wuce gona da iri da rigakafin yaki.”

“Ita ma kasar Faransa ta fitar da sanarwar, inda ta jaddada cewa kasashe biyar din sun jaddada aniyarsu na sarrafa makaman kare dangi da kuma daura damara. Za su ci gaba da bin hanyoyin da za su bi wajen sarrafa makaman kare dangi da na nukiliya”, in ji shi.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da a ke samun karuwar tashe-tashen hankula na siyasa a tsakanin Rasha da kasashen yammacin Turai, saboda damuwar da Rasha ke yi game da girke sojojinta a kusa da makwabciyarta Ukraine. Moscow ta ce za ta iya zagayawa da sojojinta zuwa yankinta kamar yadda ta ga ya dace.

 

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp