fidelitybank

Ba za a iya samun asara a yakin makan kare dangi ba – Kasashen Ketare

Date:

Kasashen China da Rasha da Birtaniya da Amurka da Faransa sun amince cewa ya kamata a kaucewa ci gaba da yaduwar makaman kare dangi da kuma yakin nukiliya.

A cewar sanarwar hadin gwiwa da kasashe biyar masu karfin makamin nukiliyar da fadar Kremlin ta wallafa a ranar Litinin.

Ta ce kasashen biyar wadanda su ne mambobi na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, sun dauki alhakinsu na farko na kaucewa yaki tsakanin kasashen da ke amfani da nukiliya da kuma rage hadarurruka, yayin da su ke da niyyar hada kai da dukkan kasashen wajen domin samar da yanayi na tsaro.

“Mun ayyana cewa ba za a iya samun nasara a yakin makaman kare dangi ba na nukiliya, bai kamata a fara shi ba,” in ji sanarwar da yaren Rasha.

“Kamar yadda amfani da makaman nukiliya zai haifar da sakamako mai nisa, muna kuma tabbatar da cewa makaman nukiliya – muddun akwai su – ya kamata su yi aiki da manufofin kariya, da hana wuce gona da iri da rigakafin yaki.”

“Ita ma kasar Faransa ta fitar da sanarwar, inda ta jaddada cewa kasashe biyar din sun jaddada aniyarsu na sarrafa makaman kare dangi da kuma daura damara. Za su ci gaba da bin hanyoyin da za su bi wajen sarrafa makaman kare dangi da na nukiliya”, in ji shi.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da a ke samun karuwar tashe-tashen hankula na siyasa a tsakanin Rasha da kasashen yammacin Turai, saboda damuwar da Rasha ke yi game da girke sojojinta a kusa da makwabciyarta Ukraine. Moscow ta ce za ta iya zagayawa da sojojinta zuwa yankinta kamar yadda ta ga ya dace.

 

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp