fidelitybank

Ba za a iya samun asara a yakin makan kare dangi ba – Kasashen Ketare

Date:

Kasashen China da Rasha da Birtaniya da Amurka da Faransa sun amince cewa ya kamata a kaucewa ci gaba da yaduwar makaman kare dangi da kuma yakin nukiliya.

A cewar sanarwar hadin gwiwa da kasashe biyar masu karfin makamin nukiliyar da fadar Kremlin ta wallafa a ranar Litinin.

Ta ce kasashen biyar wadanda su ne mambobi na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, sun dauki alhakinsu na farko na kaucewa yaki tsakanin kasashen da ke amfani da nukiliya da kuma rage hadarurruka, yayin da su ke da niyyar hada kai da dukkan kasashen wajen domin samar da yanayi na tsaro.

“Mun ayyana cewa ba za a iya samun nasara a yakin makaman kare dangi ba na nukiliya, bai kamata a fara shi ba,” in ji sanarwar da yaren Rasha.

“Kamar yadda amfani da makaman nukiliya zai haifar da sakamako mai nisa, muna kuma tabbatar da cewa makaman nukiliya – muddun akwai su – ya kamata su yi aiki da manufofin kariya, da hana wuce gona da iri da rigakafin yaki.”

“Ita ma kasar Faransa ta fitar da sanarwar, inda ta jaddada cewa kasashe biyar din sun jaddada aniyarsu na sarrafa makaman kare dangi da kuma daura damara. Za su ci gaba da bin hanyoyin da za su bi wajen sarrafa makaman kare dangi da na nukiliya”, in ji shi.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da a ke samun karuwar tashe-tashen hankula na siyasa a tsakanin Rasha da kasashen yammacin Turai, saboda damuwar da Rasha ke yi game da girke sojojinta a kusa da makwabciyarta Ukraine. Moscow ta ce za ta iya zagayawa da sojojinta zuwa yankinta kamar yadda ta ga ya dace.

 

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp