fidelitybank

Artabu: ‘Yan ta’adda 38 sun mutu ciki harda ‘yan sanda 5 – ‘Yan Sanda

Date:

Akalla ‘yan ta’adda 38 ne a ke zargi an kashe yayin da jami’an ‘yan sanda biyar su ka rasa ransu a wani arangama da a ka yi da juna daban-daban a jihar Katsina a shekarar 2021.

Kwamishinan ‘yan sanda jihar Katsina, Sanusi Buba ya bayyana hakan ne yayin wani taron ‘yan jarida na musamman.

Kwamishinan wanda ya samu wakilcin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya koka da ayyukan ‘yan ta’adda a jihar.

Ya ce “Hakika, ba shakka lokaci ne mai wahala, rundunar ta samu gagarumar nasara a kan barazanar ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da makami da sauran nau’ikan laifuka da aikata laifuka a jihar. Shekarar 2021 ta samu a cikin raguwar yawan laifuka a jihar idan a ka kwatanta da shekarar da ta gabata.”

“A yayin wannan artabun, an kashe ‘yan bindiga talatin da takwas (38) a fadan bindigu daban-daban yayin da jami’an ‘yan sanda biyar (5) suka biya su ka rasa ransu,” inji shi.

Kwamishinan ya ce, rundunar ta kama mutane 999 da a ke zargi da aikata laifuka 608 da a ka samu. Yayin da adadin wadanda a ka kama 874 ke fuskantar shari’a a kotunan shari’a daban-daban na jihar.

Ya kara da cewa an kama jimillar mutane 157 da a ke zargin ‘yan fashi da makami ne, sannan 145 daga cikinsu an gurfanar da su gaban kotu yayin da 12 ke ci gaba da bincikar su.

“An kama masu garkuwa da mutane sittin da biyar sannan an gurfanar da 63 a gaban kotu yayin da biyu ke kan bincike.”

Ya kuma ce,”An kama mutane 244 da a ke zargin barayin shanu ne, daga cikinsu an gurfanar da wadanda a ke zargin 230 a gaban kotu yayin da 14 ke ci gaba da bincikar su. An kwato dabbobin gida guda 1,243 wadanda su ka hada da shanu 867, tumaki 352, awaki 24 da jaki daya daga cikin mazubin”. A cewar sanarawar.

Kwamishinan ya ce an kama mutane 246 da ake zargi a cikin 195 da aka samu na fyade da kuma laifukan da suka saba wa ka’ida inda ya ce an kubutar da mutane 63 da aka yi garkuwa da su a wasu shari’o’i hudu da aka samu na fataucin bil adama da aka kai ofishin NAPTIP na jihar Kano.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp