fidelitybank

Artabu: ‘Yan ta’adda 38 sun mutu ciki harda ‘yan sanda 5 – ‘Yan Sanda

Date:

Akalla ‘yan ta’adda 38 ne a ke zargi an kashe yayin da jami’an ‘yan sanda biyar su ka rasa ransu a wani arangama da a ka yi da juna daban-daban a jihar Katsina a shekarar 2021.

Kwamishinan ‘yan sanda jihar Katsina, Sanusi Buba ya bayyana hakan ne yayin wani taron ‘yan jarida na musamman.

Kwamishinan wanda ya samu wakilcin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya koka da ayyukan ‘yan ta’adda a jihar.

Ya ce “Hakika, ba shakka lokaci ne mai wahala, rundunar ta samu gagarumar nasara a kan barazanar ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da makami da sauran nau’ikan laifuka da aikata laifuka a jihar. Shekarar 2021 ta samu a cikin raguwar yawan laifuka a jihar idan a ka kwatanta da shekarar da ta gabata.”

“A yayin wannan artabun, an kashe ‘yan bindiga talatin da takwas (38) a fadan bindigu daban-daban yayin da jami’an ‘yan sanda biyar (5) suka biya su ka rasa ransu,” inji shi.

Kwamishinan ya ce, rundunar ta kama mutane 999 da a ke zargi da aikata laifuka 608 da a ka samu. Yayin da adadin wadanda a ka kama 874 ke fuskantar shari’a a kotunan shari’a daban-daban na jihar.

Ya kara da cewa an kama jimillar mutane 157 da a ke zargin ‘yan fashi da makami ne, sannan 145 daga cikinsu an gurfanar da su gaban kotu yayin da 12 ke ci gaba da bincikar su.

“An kama masu garkuwa da mutane sittin da biyar sannan an gurfanar da 63 a gaban kotu yayin da biyu ke kan bincike.”

Ya kuma ce,”An kama mutane 244 da a ke zargin barayin shanu ne, daga cikinsu an gurfanar da wadanda a ke zargin 230 a gaban kotu yayin da 14 ke ci gaba da bincikar su. An kwato dabbobin gida guda 1,243 wadanda su ka hada da shanu 867, tumaki 352, awaki 24 da jaki daya daga cikin mazubin”. A cewar sanarawar.

Kwamishinan ya ce an kama mutane 246 da ake zargi a cikin 195 da aka samu na fyade da kuma laifukan da suka saba wa ka’ida inda ya ce an kubutar da mutane 63 da aka yi garkuwa da su a wasu shari’o’i hudu da aka samu na fataucin bil adama da aka kai ofishin NAPTIP na jihar Kano.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp